Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiGwamnatin Jigawa ta kori wasu masu samar da abincin azumi 22 kan...

Gwamnatin Jigawa ta kori wasu masu samar da abincin azumi 22 kan zargin badakala a shirin ciyarwar watan Ramadan

Gwamnatin jihar Jigawa ta sallami wasu masu samar da abinci guda 22 da ke cikin shirin rabon abinci na watan Ramadan bisa zargin yaudara, rashin gaskiya da kuma wasu zarge-zargen almundahana wajen tafiyar da kudade.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa matakin na daga cikin yunkurin gwamnati na tabbatar da gaskiya da rikon amana a shirin da aka kaddamar domin ciyar da talakawa da marasa ƙarfi a watan Ramadan na shekarar 2026.

Gwamnan jihar, Umar Namadi, ne ya kaddamar da shirin wanda ke da niyyar ciyar da mutane kusan miliyan 7.9 a cibiyoyi 640 da aka ware domin rabon abinci a fadin jihar.

Sai dai rahotanni sun nuna cewa bayan kusan makonni biyu da fara shirin, bincike da sa ido da aka gudanar tare da koke-koken jama’a sun gano wasu manyan laifuffuka daga wasu masu samar da abincin.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata