Gwamnatin jihar Jigawa ta sallami wasu masu samar da abinci guda 22 da ke cikin shirin rabon abinci na watan Ramadan bisa zargin yaudara, rashin gaskiya da kuma wasu zarge-zargen almundahana wajen tafiyar da kudade.
Jaridar Punch ta ruwaito cewa matakin na daga cikin yunkurin gwamnati na tabbatar da gaskiya da rikon amana a shirin da aka kaddamar domin ciyar da talakawa da marasa ƙarfi a watan Ramadan na shekarar 2026.
Gwamnan jihar, Umar Namadi, ne ya kaddamar da shirin wanda ke da niyyar ciyar da mutane kusan miliyan 7.9 a cibiyoyi 640 da aka ware domin rabon abinci a fadin jihar.
Sai dai rahotanni sun nuna cewa bayan kusan makonni biyu da fara shirin, bincike da sa ido da aka gudanar tare da koke-koken jama’a sun gano wasu manyan laifuffuka daga wasu masu samar da abincin.
