Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiGwamnatin jihar Bayelsa ta umurci binciken gawar mataimakin gwamnnan domin gano musabbabin...

Gwamnatin jihar Bayelsa ta umurci binciken gawar mataimakin gwamnnan domin gano musabbabin mutuwar fuju’arsa

Gwamnan Jihar Bayelsa, Sanata Douye Diri, ya bayar da umarnin a gudanar da bincike (autopsy) kan gawar marigayi mataimakinsa, Sanata Lawrence Ewhrudjakpo, domin gano ainihin musabbabin mutuwarsa.

Gwamna Diri ya bayyana hakan ne a ranar Asabar yayin da tsohon Shugaban Nijeriya, Dr Goodluck Jonathan, ya kai masa ziyarar ta’aziyya a fadar gwamnati da ke Yenagoa.

Diri ya ce umarnin ya zama dole ne sakamakon jita-jita da ke yawo a kafafen sada zumunta game da mutuwar mataimakin gwamnan kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

A nasa bangaren, Jonathan ya bayyana mutuwar Ewhrudjakpo a matsayin babban rashi ga al’ummar Bayelsa, yana mai cewa marigayin ya kasance mutum mai himma da aminci, wanda ya wakilci gwamnan jihar a shirye-shiryen Gidauniyar Jonathan, ciki har da taron Democracy Dialogue da aka gudanar a Benin, Jihar Edo.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata