Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiGwamnatin jihar Lagos ta fara gwajin lafiya ga maniyyata aikin hajjin 2026

Gwamnatin jihar Lagos ta fara gwajin lafiya ga maniyyata aikin hajjin 2026

Gwamnatin Jihar Lagos ta fara aikin duba lafiyar dukkan maniyyatan da ke shirin halartar aikin Hajjin shekarar 2026 a kasar Saudiyya. Sakataren Hukumar Jin Dadin Maniyyata Musulmi ta jihar, AbdulHakeem Ajomagberin, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa.

Sanarwar, wadda Mataimakin Daraktan Hulda da Jama’a Taofeek Lawal ya sanya wa hannu, ta ce za a gudanar da aikin duba lafiyar daga Laraba 14 zuwa Asabar 24 ga Janairu, 2026, a cibiyoyi goma da aka tanada a fadin jihar Lagos, karkashin jagorancin Dr. Mazeedat Erinosho.

Ajomagberin ya bayyana cewa an rarraba kananan hukumomi zuwa cibiyoyin gwaji daban-daban domin saukaka wa maniyyata. Ya gargadi cewa duk maniyyacin da ya kasa halartar aikin duba lafiyar ba zai samu bizar shiga Saudiyya ba.

Haka kuma, hukumar ta nada jami’an jadawalin kananan hukumomi domin kula da jin dadin maniyyata kafin tafiya da kuma yayin aikin Hajji. Ajomagberin ya jaddada cewa gwamnatin jihar ba za ta lamunci duk wani abu da zai kawo cikas ga nasarar aikin Hajji ba, yana mai bukatar jami’an da aka nada su nuna gaskiya da jajircewa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata