Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiGwamnatin Lagos ta kama ’yan daba 281 dake hantarar matafiya kan hanya

Gwamnatin Lagos ta kama ’yan daba 281 dake hantarar matafiya kan hanya

Gwamnatin Jihar Lagos ta sanar da kama ƴan daba 281 da ake kira Omotaku a kokarin da take ci gaba da yi na dawo da tsaro da daidaito a wuraren jama’a a fadin jihar.

Kwamishinan Muhalli da Albarkatun Ruwa na jihar, Tokunbo Wahab, ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Asabar, inda ya ce an riga an gurfanar da wadanda aka kama a gaban kotu.

Sanarwar ta ce aikin, wanda ya dauki tsawon mako guda, rundunar Taskforce ta jihar ta gudanar da shi a wurare da dama, ciki har da Lekki Phase 1, Ikoyi, Lekki–Ajah Expressway, Bourdillon, Akowonjo Road, Egbeda, Fadeyi, Costain, Funsho Williams Avenue, Victoria Island, Apongbon, Jibowu, Yaba, Lagos Island, Palmgrove, Ojuelegba da Surulere, da sauran hanyoyi a bangaren tsibiri da kuma babban birnin jihar.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata