Tsohon mataimakin majalisar dattawan Nijeriyar na fuskantar daurin shekaru 9 a gidan yarin Birtaniya, bayan samun sa da laifin siyan sassan jikin dan Adam.
Daily Trust ta ruwaito cewa gwamnatin Nijeriya ta aike da tawaga ta musamman, wadda ta hada da ministan harkokin waje Ambasada Yusuf Tuggar da kuma ministan shari’a Lateef Fagbemi SAN domin tattaunawa da hukumomin Birtaniya.
Majiyoyi sun tabbatar da cewa wannan yunkuri na daga cikin bukatar shugaba Tinubu na neman a saki Ekeremadu da wuri, ko kuma sake bibiyar hukuncin da aka yanke masa, ta hanyar bin tsarin dokokin shari’a da ‘yancin dan Adam.
