Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiGwamnatin Nijeriya ta dakatar da ziyarar ibada ta Kiristoci zuwa Isra’ila

Gwamnatin Nijeriya ta dakatar da ziyarar ibada ta Kiristoci zuwa Isra’ila

Gwamnatin Nijeriya ta sanar da dakatar da duk wata ziyara ta Kirista zuwa Isra’ila sakamakon halin tsaro a Gabas ta Tsakiya.

Hukumar kula da ziyarar ibada ta Kiristoci a Nijeriya (NCPC) ta bayyana hakan ta bakin Sakataren Zartarwarta, Bishop Stephen Adegbite, a wata sanarwa da aka fitar an Abuja.

Hukumar ta ce matakin ya biyo bayan ayyana dokar ta-baci an Israel, tare da jaddada cewa tsaro da jin dadin mahajjata su ne a gaba. Dakatarwar ta shafi har da shirye-shiryen da kamfanoni masu zaman kansu ke gudanarwa har sai lamarin ya daidaita.

NCPC ta kuma bayyana cewa ta kammala aikin babban ziyarar 2025 zuwa Isra’ila da Jordan, inda rukuni na karshe ya iso lafiya a filin jirgin saman Murtala Muhammed a ranar 3 ga Maris.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata