Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiGwamnatin Nijeriya ta dauki hayar kamfani a Amurka domin kare ta game...

Gwamnatin Nijeriya ta dauki hayar kamfani a Amurka domin kare ta game da zargin cin zarafin Kiristoci kan Dala miliyan 9 – Daily Trust

Gwamnatin Nijeriya ta kulla yarjejeniya da wani kamfanin Amurka kan dala miliyan 9 domin bayyana kokarinta na kare Kiristoci da kuma tabbatar da goyon bayan Amurka a yaki da ta’addanci.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, takardun Ma’aikatar Shari’a ta Amurka sun nuna cewa kamfanin Aster Legal ya dauki DCI Group a madadin Mai Ba Shugaban Kasa Shawara kan Tsaro, Nuhu Ribadu, inda aka sanya hannu kan yarjejeniyar a ranar 17 ga Disamba, 2025.

Yarjejeniyar za ta dauki watanni shida, Nijeriya ta biya dala miliyan 4.5 tun farko, kuma ana biyan dala 750,000 duk wata. Matakin ya zo ne a lokacin da ake samun takaddama tsakanin Nijeriya da Amurka kan zargin cin zarafin Kiristoci, zargin da gwamnatin Nijeriya ta musanta.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata