Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiGwamnatin Nijeriya za ta kafa kwalejin koyon likitanci ta sojoji don magance...

Gwamnatin Nijeriya za ta kafa kwalejin koyon likitanci ta sojoji don magance karancin likitoci

Gwamnatin Nijeriya ta sanar da shirin kafa kwalejin koyon likitanci ta soji “Armed Forces College of Medicine and Health Sciences” a matsayin wani mataki na dakile karancin likitoci da cike giɓin likitoci 340,000 a Nijeriya.

Shirin ya biyo bayan taron ministoci da suka haɗa da ministan ilimi Dr. Maruf Tunji Alausa, karamar minstar ilimi Suwaiba Ahmed, da ministan tsaro, Christopher Musa, tare da sauran masu ruwa da tsaki a fannin ilimi, lafiya da tsaro.

Kwalejin za ta zama wata hanya ta ƙarfafa ayyukan kiwon lafiya na sojoji, horar da likitoci da masu jinya, masu kwarewa wajen kula da masu raunin a wajen yaki, da kuma samar da karin likitoci a fadin ƙasa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata