Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiGwamnatin Sokoto ta nesanta kanta da kyautar mota da shago da aka...

Gwamnatin Sokoto ta nesanta kanta da kyautar mota da shago da aka bai wa Rahama Saidu

Gwamnatin jihar Sokoto ta bayyana cewa ba ta da wata alaƙa da batun bai wa ƴar TikTok Rahama Saidu mota da shago, wanda wani mai suna Sanin Jaman ya yi, a wani faifan bidiyo ya karade kafafen sada zumunta.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Ofishin Mai Magana da yawun Gwamnan jihar Sokoto, Ahmad Aliyu, ya fitar a ranar Lahadi.

Sanarwar ta ce, Sanin Jaman ya bayyana cewa kyautar da ya bai wa Rahama Saidu a kashin kansa ne, domin nuna godiya da yabon da take yi wa gwamnatin Ahmad Aliyu a jihar Sokoto.

Sai dai gwamnatin jihar ta jaddada cewa ba ta da hannu ko alaƙa da wannan kyauta, tare da nesanta Gwamna Ahmad Aliyu da gwamnatin jihar Sokoto daga lamarin baki ɗaya.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata