Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiGwamnatin Tanzaniya ta umurci ma’aikata su yi aiki daga gida, bayan rikicin...

Gwamnatin Tanzaniya ta umurci ma’aikata su yi aiki daga gida, bayan rikicin zabe

Gwamnatin kasar Tanzaniya ta umurci dukkan ma’aikatan gwamnati su ci gaba da yin aiki daga gida, yayin da ta kuma shawarci masu aikin kamfanoni masu zaman kansu su ba ma’aikatansu dama su yi aiki daga gida.

DW Africa ta rawaito cewa, a wani sako da sakataren ma’aikatar yada labarai ta Tanzaniya, ya wallafa a shafinsa na Instagram, inda ya nemi ‘yan kasar su gudanar da harkokinsu daga gida saboda halin da ake ciki.

Wannan umarni ya zo ne bayan da gwamnati ta kakaba dokar hana fita da a Dar es Salaam sakamakon tashin hankali da ya biyo bayan rikicin zaɓe da ya barke a ranar Laraba.

Rahotanni sun bayyana cewa an dauki wannan mataki ne domin tabbatar da tsaro da kare rayuka da dukiyoyin jama’a yayin da hukumomi ke kokarin dawo da zaman lafiya a babban birnin ƙasar.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata