Monday, April 6, 2026
HomeSiyasaGwamnatin Tinubu na tuhumar Stella Oduah, da cin hancin ₦5bn

Gwamnatin Tinubu na tuhumar Stella Oduah, da cin hancin ₦5bn

Tsohuwar Ministar Sufurin Jiragen Saman Nijeriya, Stella Oduah, ta gurfanar a gaban kotu Abuja ranar Laraba kan zargin cin hanci da rashawa na biliyan 5

An shigar da kara ne bisa laifuka biyar da suka shafi yaudara, ciki har da samun ₦2.4 biliyan daga Ma’aikatar Sufurin Jiragen Sama ta kamfanin Broad Waters Resources da ikirarin kudin na kula da aikin fasaha ne.

Kodayake Oduah da abokin laifinta, Gloria Odita, sun musanta dukkan tuhumar.

Alkalin kotu, Justice Hamza Muazu, ya ba Oduah belin kanta da kanta, tare da rike fasfo dinsu, sannan ya haramta mata fita daga ƙasar ba tare da izinin kotu ba.

Wannan shi ne karo na biyu gwamnatin tarayya ke gurfanar da Oduah kan wannan batu, bayan karar farko da EFCC ta shigar a kotun ta Abuja an janye ta.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata