Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiGwamnatin Yobe ta sassauta dokar hana fitar dare

Gwamnatin Yobe ta sassauta dokar hana fitar dare

Mai ba Gwamnan jihar shawara kan harkokin tsaro, Dahiru Abdulsalam, ne ya bayyana hakan ga manema labarai bayan taron tsaro da mataimakin Gwamnan jihar, Idi Barde Gubana, ya jagoranta.

A cewarsa, kwamitin tsaron jihar ya ga dacewar sassauta dokar ne domin bai wa Musulmi damar gudanar da ayyukan addini cikin sauƙi a lokacin azumi.

Ya bayyana cewa an kira taron tsaron ne domin tantance yanayin tsaro a faɗin jihar, tare da tabbatar da cewa al’umma sun gudanar da kwanaki 30 na azumi cikin lumana, tare da kare rayuka da dukiyoyinsu yadda ya kamata.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata