Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiSama da mutum 170 ne ke son zama ’yan Nijeriya daga kasashen...

Sama da mutum 170 ne ke son zama ’yan Nijeriya daga kasashen ketare – Ministan cikin gida

Ministan cikin gida, Olubunmi Tunji Ojo, ya bayyana cewa sama da ’yan kasashen ketare 170 ne suke neman zama ’yan Nijeriya.

Tunji Ojo ya sanar da hakan ne a shafinsa na X, bayan ya jagoranci taron Citizenship Advisory Committee a Abuja.

A cewarsa, an kafa kwamitin ne domin duba da kuma ba da shawarar neman zama dan Nijeriya ga masu bukata domin amincewa.

Kwamitin ya kunshi manyan jami’an gwamnati daga ma’aikatun Shari’a, harkokin kasashen waje, hukumar tsaro ta DSS, da hukumar shige da fice ta NIS.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata