Wednesday, April 8, 2026
HomeLabaraiHukumar EFCC a Nijeriya ta samu nasarar karɓe kadara mafi girma tun...

Hukumar EFCC a Nijeriya ta samu nasarar karɓe kadara mafi girma tun bayan kafa hukumar zuwa yanzu

Kotu ta sahalewa hukumar EFCC mai yaƙi da cin hanci da rashawa a Nijeriya ta karɓe wani rukunin gidaje 731 dake birnin Abuja, daga wani tsohon ƙusa a cikin gwamnatin tarayya wanda hukumar ba ta bayyana sunansa ba.
Mai Shari’a Justice Jude Onwuegbuzie ne ya bayarda umurnin a cikin hukuncin da ya yanke a yau, a cewar sanarwar da hukumar ta wallafa a shafinta na Facebook.
Rukunin gidajen dake a yankin Cadastral Zone C09, Gundumar Lokogoma, a Abuja, a yanzu kotu ta hannunta su ga gwamnatin tarayya.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata