Tuesday, April 7, 2026
HomeLabaraiHukumar EFCC ta fara kwato kuɗaɗen da kamfanin CBEX ya tatuke ‘yan Nijeriya

Hukumar EFCC ta fara kwato kuɗaɗen da kamfanin CBEX ya tatuke ‘yan Nijeriya

Hukumar EFCCC mai yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, ta ce ta kwato wasu kudade daga kamfanin zuba jarin bogi na CBEX.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito yadda dubban ‘yan Najeriya da suka saka hannun jari a dandalin suka yi asarar kimanin Naira tiriliyan 1.3.

CBEX dai ya rika bai wa masu saka hannun jarin ribar kashi 100 cikin 100 a cikin kwanaki 30, kafin daga bisani ya gudu da kudaden mutanen.

Da yake magana a gidan Talabijin na TVC, shugaban hukumar EFCC Ola Olukoyede, ya cewa hukumar ta EFCC ta kama wasu da ake zargin suna damfarar CBEX, yana mai cewa hukumar na ci gaba da bin diddigin wasu da suka gudu.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata