Sunday, April 5, 2026
HomeWasanniHukumar FIFA ta ci tarar kungiyoyin kwallon kafar Nijeriya da DR Congo

Hukumar FIFA ta ci tarar kungiyoyin kwallon kafar Nijeriya da DR Congo

Hukumar ƙwallon ƙafa ta duniya, FIFA, ta ci tarar kungiyoyin kwallon kafar Nijeriya da DR Congo saboda wasu laifuka da suka faru yayin wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta 2026.

Hukumar ta ce magoya bayan ƙasashen biyu sun aikata abubuwan da suka saɓa da dokokin ta a wasan share fage na nahiyar Afirka.

A wasan, tawagar Super Eagles ta sha kashi a hannun DR Congo da ci 4–3 a bugun fenariti, bayan an tashi 1–1 bayan ƙarin lokaci.

Rahoton ladabtarwa na FIFA ya nuna cewa an ci tarar Najeriya ne saboda rashin tsaro da kuma jefa abubuwa cikin fili daga bangaren magoya baya, wanda ya saɓa da sashe na 17.2.b na dokokin ladabtarwa.

Ita kuwa DR Congo an hukunta ta ne sakamakon amfani da na’urar laser daga bangaren magoya bayanta domin haske ’yan wasan Najeriya, wanda ya saba wa sashe na 17.2.c na dokokin.

A hukuncin da ta yanke, FIFA ta ci tarar Najeriya franc na Switzerland 1,000, yayin da ta ci DR Congo franc 5,000.

Nasarar da DR Congo ta samu a kan Najeriya ta ba ta damar tsallakawa zuwa wasan neman tikitin shiga gasar ta duniya da za a buga a kasar Mexico a karshen wannan wata.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata