Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiHukumar FRSC ta bayyana dalilan yawan afkuwar hadura a titunan Nijeriya

Hukumar FRSC ta bayyana dalilan yawan afkuwar hadura a titunan Nijeriya

Hukumar kiyaye afkuwar hadura ta Nijeriya FRSC ta bayyana cewa a mafiya yawan lokuta rashin hakuri, gudun wuce sa’a tare da karya dokokin hanya ne ke haifar da hadura a titunan kasar.

Kwamandan hukumar na yankin Okitipupa a jihar Ondo shi ne ya bayyana haka, yayin wani taron wayar da kai game da zirga-zirgar ababen hawa a lokacin bukukuwan karshen shekara.

Hukumar ta kuma nuna damuwa da cewa an fi samun ire-iren wadannan hadurra a watannin karshen shekara da ake samun bukukuwa a cikin su, kamar yadda The Nation ta ruwaito.

 

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata