Sunday, April 5, 2026
HomeKetareHukumar lafiya ta duniya ta koka kan irin kudaden da ake kashewa...

Hukumar lafiya ta duniya ta koka kan irin kudaden da ake kashewa a yake-yake duk da yunwar da ake fama da ita a fadin duniya

Babban Daraktan Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO, Tedros Adhanom Ghebreyesus, ya soki yadda kasashen duniya ke kashe makudan kudade wajen yaki, yana mai cewa hakan na nuna cewa an karkatar da muhimmancin abubuwan da ya kamata a ba fifiko a kai.

A wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, ya ce kudaden da ake kashewa kan harkokin soja a duniya sun kai dala tiriliyan 2.7 a cikin shekara guda, alhali kiyasin MDD ya nuna cewa dala biliyan 93 kacal ake bukata a duk shekara domin kawo karshen yunwa a duniya nan da shekarar 2030.

Ya ce hakan na nufin kasashen duniya na kashe kusan sau 30 fiye da haka wajen yaki da juna maimakon tabbatar da cewa kowa ya samu abinci, yana mai cewa wannan bambanci na nuna gazawar duniya wajen tinkarar matsalar yunwa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata