Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiHukumar NDLEA ta kama buhunnan tabar wiwi 64 a Kano

Hukumar NDLEA ta kama buhunnan tabar wiwi 64 a Kano

Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi (NDLEA) reshen Kano ta kama buhuna 64 na tabar wiwi da aka boye a cikin wata tirelar siminti a kan titin Kano–Zariya. Kakakin rundunar, ASN Sadiq Maigatari, ya ce an kama kayan ne ranar 2 ga Fabrairu, 2026, bayan samun bayanan sirri da sa ido na musamman.

Ya ce tirelar dauke da simintin Dangote ta taso daga Obajana a Jihar Kogi zuwa Mubi a Adamawa, kafin jami’ai su tsaida ta a kan titin Zariya–Kano. An kama direban motar, wanda ke hannun hukuma domin ci gaba da bincike.

Kwamandan NDLEA na Kano, D.Y. Lawal, ya ce an boye miyagun kwayoyin cikin kaya na halal, kuma ana zargin an shirya rarraba su ne a Kano gabanin watan Ramadan. Ya jaddada cewa ba za su bari masu fatauci su lalata al’umma ba.

Hukumar ta ce za ta kara tsaurara sintiri da bincike a fadin jihar, tare da bin diddigin wadanda ke da hannu a lamarin domin gurfanar da su a gaban kuliya. Ta kuma bukaci jama’a su rika bayar da bayanai kan duk wata alama ta fataucin miyagun kwayoyi.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata