Monday, April 6, 2026
HomeWasanniHukumar NFF ta ce za ta biya bashin da kocin Super Eagles...

Hukumar NFF ta ce za ta biya bashin da kocin Super Eagles ke binta

Wani babban jami’in hukumar NFF ya bayyana cewa za a biya kocin Super Eagles, Eric Chelle, albashin watanni uku da yake bi, yayin da Najeriya ke shirin shiga gasar AFCON 2025 a Morocco.
An ruwaito cewa Chelle yana bin hukumar ta NFF albashin fiye da watanni uku, kafin fara gasar da za a yi daga 21 ga Disamba zuwa 18 ga Janairu 2026.
Inda Najeriya za ta fitar da jerin ‘yan wasa 28 da za su halarci gasar tsakanin yau da Alhamis.
Jami’in hukumar ta NFF ya tabbatar wa jaridar The PUNCH cewa za a biya Chelle nan kusa.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata