Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiHukumar tace fina-finai ta Kano ta soke lasisin wani gidan gala bisa...

Hukumar tace fina-finai ta Kano ta soke lasisin wani gidan gala bisa dalilai na tsaro

Hukumar Tace Fina-finai ta Jihar Kano ta soke lasisin gudanar da ayyukan wani gidan gala mai suna Sunsiro Entertainment, wanda ke kan titin Yahaya Gusau, Sharada, Kano.

Daukar matakin ya biyo bayan samun korafe-korafe kan tarbiyya tare da sahihan rahotannin tsaro daga al’ummar yankin da abin ya shafa.

A cikin wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na hukumar Abdullahi Sani Sulaiman ya fitar, ya bayyana cewa shugaban hukumar, Abba El-Mustapha, ya amince da matakin ne bisa ga sakamakon binciken da ke kunshe a cikin rahoton ’yan sanda da kuma shawarwarin da kwamitin sa ido na hukumar ya gabatar.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata