Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiHukumomin kasar Madagascar sun kama mutane biyu 'yan kasar waje bisa zargin...

Hukumomin kasar Madagascar sun kama mutane biyu ‘yan kasar waje bisa zargin kitsa juyin mulki

Hukumomin kasar ta Madagascar sun ce an kama mutanen biyu ne ‘yan kasar waje a kasar biyo bayan zargin da ake musu da yunkurin kitsa wa shugaban kasar Michael Mandrianirina juyin mulki.

Wannan zargi ya biyo bayan wani bincike da hukumomin leken asiri ta kasar Madagascar ta kaddamar kamar yadda sabon babban darakta janar dinta Rufin Tolojara Lebiria ya sanar a yayin wani taron manema labarai.

Mutanen biyu da ba a bayyana kasar su ta asali ba ‘yan kasuwa ne da ke zaune a kasar sun dauki a kalla shekaru biya, kuma binciken da aka yi a wata babbar masana’antar daya daga cikin su ya sa an gano kudin da ya kai kwatankwacin Euro 385,000 da wadansu tarin makamai.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata