Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiIna da ƙwarin gwiwar lashe zaɓen gwamnan jihar Ogun a zaɓen 2027...

Ina da ƙwarin gwiwar lashe zaɓen gwamnan jihar Ogun a zaɓen 2027 – Iyabo Obasanjo

Tsohuwar Sanata mai wakiltar Ogun ta tsakiya Iyabo Obasanjo, ta bayyana cewa tana da kwarin gwiwar lashe zaben gwamnan jihar Ogun a 2027, tana mai cewa ita ce ‘yar takara mafi ƙarfi a fafatawar.

Gidan talabijin na Channels ya ruwaito cewa Iyabo Obasanjo ta bayyana hakan ne a wata hira da ta yi, inda ta yi magana kan dawowarta siyasa, burinta na zama gwamna da kuma goyon bayan da take sa ran samu daga iyalanta.

Ta ce tana da yakinin cewa iyayenta, ciki har da tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo, za su zabe ta idan ta tsaya takara, ta ce a matsayinta na mace mai kusan shekaru 60, tana ganin ta yi sa’a kasancewar har yanzu tana da iyaye biyu da rai.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata