Shugaban majalisar dattawan Nijeriya Sanata Godswill Akpabio, ya ce gwamnati na da nauyin dawo da zaman lafiya a jihar Filato da Nijeriya baki ɗaya a wuyanta, yana mai jaddada cewa ba wata ƙasa da za ta kawo wa ƙasar zaman lafiya sai ‘yan Nijeriya da kansu.
Jaridar Daily Trust, ta ruwaito Akpabio na yin wannan bayani ne ranar Asabar a Jos yayin taron tarbar sababbin ‘yan wadanda suka koma jam’iyyar APC.
Akphabio ya ce Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya kuduri aniyar magance matsalar rashin tsaro da ta addabi Filato da wasu sassan ƙasar.
Akpabio ya bayyana damuwarsa kan yadda rikici da zubar da jini suka dade suna addabar jihar tun daga shekarar 2010, yana mai cewa duk lokacin da ya ji an hallaka mutum, ko yaro ne ko babba idanunsa na cika da hawaye.
