Kwamitin gudanarwa na jam’iyyar PDP da ke karkashin jagorancin Tanimu Turaki, ya bayyana cewa Hukumar zaben Nijeriya INEC, ba ta da hurumin zaɓar shugabanci ko tsoma baki a harkokin cikin gida na jam’iyyar.
Sakataren yada labarai na kasa na PDP, Ini Ememobong, ne ya bayyana hakan yayin martani kan taron da INEC ta yi da jam’iyyun siyasa, wanda kwamitin rikon kwarya da Abdulrahman Mohammed ke jagoranta ya halarta a madadin PDP.
Ememobong ya ce duk da cewa INEC ta gayyaci shugabannin jam’iyyu, gayyatar wasu tsofaffin ‘ya’yan PDP da ke ikirarin jagorantar wani kwamitin rikon kwarya ya sabawa kundin tsarin mulkin jam’iyyar, domin babu irin wannan tanadi a cikinsa.
