Sunday, April 5, 2026
HomeSiyasaINEC ta yi watsi da shugabancin PDP tsagin Tanimu Turaki

INEC ta yi watsi da shugabancin PDP tsagin Tanimu Turaki

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa ba za ta amince da Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa (NWC) na jam’iyyar PDP da Kabiru Turaki ke jagoranta ba, bisa dalilin hukuncin kotu da ke nan daram da kuma batutuwan shari’a da har yanzu ba a kammala ba.

INEC ta bayyana hakan ne a cikin wata wasiƙa mai kwanan wata 22 ga Disamba, 2025, wadda Sakatariyar hukumar, Dakta Rose Oriaran-Anthony, ta sanya wa hannu. Hukumar ta ce ta karɓi buƙatu daga lauyoyin PDP na neman a amince da kuma sabunta sunayen shugabannin jam’iyyar da aka ce an zaɓa a babban taron ƙasa da aka yi a Ibadan, Jihar Oyo, a ranakun 15 da 16 ga Nuwamba, 2025.

Sai dai INEC ta ce bayan nazari, ta gano akwai hukuncin Kotun Tarayya da ke Abuja guda biyu waɗanda suka hana hukumar sa ido, amincewa ko aiwatar da sakamakon taron PDP ɗin, har sai an bi duk umarnin kotu. Hukumar ta jaddada cewa hukuncin kotun na ƙarshe ne kuma wajibi ne ga kowa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata