Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiJami’an tsaro sun lalata abin fashewa da ’yan ta’adda suka dasa a...

Jami’an tsaro sun lalata abin fashewa da ’yan ta’adda suka dasa a Zamfara

Jami’an tsaro sun yi nasarar lalata wani abin fashewa da ake zargin ’yan ta’adda ne suka dasa a hanyar Danjibga–Kuncin Kalgo a ƙaramar hukumar Tsafe ta jihar Zamfara.

An gudanar da aikin ne ta haɗin gwiwar sashen ’yan sanda masu lalata bama-bamai (EOD–CBRN), sashen yaƙi da garkuwa da mutane, da kuma sojoji, tare da tsauraran matakan tsaro daga Rundunar ’Yan Sandan Jihar Zamfara.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, kakakin rundunar ’yan sandan jihar, Yazid Abubakar, ya ce an gudanar da aikin ne a ranar Juma’a, ƙarƙashin jagorancin SP Abdulrazak Musa Hassan.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata