Monday, April 6, 2026
HomeSiyasaJam'iyyar Accord ta bai wa Adeleke takarar gwamnan Osun

Jam’iyyar Accord ta bai wa Adeleke takarar gwamnan Osun

Jam’iyyar Accord ta ayyana gwamnan Osun Ademola Adeleke a matsayin dan takara daya tilo a zaben fidda gwanin gwamnan jihar

Kasa da sa’o’i 16 bayan Ademola Adeleke ya koma jam’iyyar Accord, shugabancin jam’iyyar na kasa ya amince da shi ya shiga zaben fidda gwani na gwamnoni.

Jaridar The Nation ta ruwaito cewa Adeleke ya sauya sheka ne da yammacin Talata tare da mataimakinsa, Kola Adewusi, da wasu manyan jami’ai.

Shugaban kwamitin tantancewa na Accord, Elder Ibe Thankgod, ya tabbatar cewa an tantance Adeleke gabanin zaben fidda gwanin da za a yi a ranar Laraba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata