Wasu rahotanni na nuni da cewa jam’iyyar APC na dab da amincewa da ci gaba da rike mukaman shugabancin jam’iyyar na ƙasa Yilwatda da sakataren ta na kasa Ajibola Basiru a taron da jam’iyyar ke shirin gudanarwa.
Jaridar Punch ta ce rahotanni daga cikin jam’iyyar sun nuna cewa manyan jiga-jigan APC na karkata ga ci gaba da riƙe waɗannan shugabanni biyu a mukamansu, ganin rawar da suka taka wajen daidaita harkokin jam’iyyar da rage rikice-rikicen cikin gida.
An ce tsarin zai taimaka wajen gujewa rigingimu masu zafi da ka iya raba kawunan jam’iyyar a gaban babban taron ƙasa.
