Wednesday, April 8, 2026
HomeSiyasaJam’iyyar Labour tsagin Julius Abure ta ba Peter Obi sa’o’i 48 ya...

Jam’iyyar Labour tsagin Julius Abure ta ba Peter Obi sa’o’i 48 ya fice daga jam’iyyar saboda shiga hadakar ADC

Jam’iyyar Labour karkashin jagorancin Julius Abure ta bai wa tsohon dan takarar shugaban kasa, Peter Obi, wa’adin sa’o’i 48 da ya fice daga jam’iyyar, bisa dalilin shiga hadakar jam’iyyun adawa da ke shirin kalubalantar APC a 2027.

A wata sanarwa da sakataren jam’iyyar na kasa, Obiora Ifoh, ya fitar a Abuja, ya ce ba su da hannu a cikin wannan hadaka, yana mai zargin cewa yawancin wadanda ke ciki suna fi ba da fifiko ga kare muradun kansu ba na jama’a ba.

Obiora ya ce jam’iyyar ba za ta lamunci kasancewa da ’yan siyasa masu fuska biyu ba, inda ya bukaci duk wani mamba da ya shiga hadakar jam’iyyun adawa da ya fice cikin sa’o’i 48 kamar yadda rahoton jaridar The Nation ya tabbatar.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata