Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiJam'iyyar PDP za ta ƙalubalanci zaɓen ƙananan hukumomin da aka gudanar a...

Jam’iyyar PDP za ta ƙalubalanci zaɓen ƙananan hukumomin da aka gudanar a Abuja

Jam’iyyar PDP ta ce ta shirya lauyoyi na musamman domin shigar da ƙorafe ƙorafe sakamakon zaɓen ƙananan hukumomin Abuja.

Jam’iyyar ta ce ta ɗauki wannan mataki ne bisa zargin an tafka kura-kurai a tsarin zaɓen tare da tsoratar da masu kaɗa ƙuri’a daga ɓangaren abokan hamayya.

A cewar PDP, rahotannin da suka samu daga wakilansu a rumfunan zaɓe sun nuna yadda aka yi katsalandan a wasu wurare, lamarin da ke iya shafar sahihancin sakamakon ƙuri’un da aka bayyana.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata