Monday, April 6, 2026
HomeSiyasaJam’iyyar SDP ta jaddada dakatarwar da ta yi ma El-Rufai na tsawon...

Jam’iyyar SDP ta jaddada dakatarwar da ta yi ma El-Rufai na tsawon shekaru 30

Kungiyar shugabannin jam’iyyar SDP na jihohi 37 ta tabbatar da cewa tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, har yanzu yana cikin dakatarwa daga jam’iyyar na tsawon shekaru 30.

Wannan sanarwa ta fito ne bayan jita-jitar da ke yawo cewa El-Rufai na shirin komawa cikin jam’iyyar kafin babban taronta na kasa.

Shugaban kungiyar, Femi Olaniyi, ya shaida wa jaridar PUNCH a ranar Lahadi an Abuja cewa, babu komawa baya a kan hukuncin da kwamitin gudanarwa na kasa ya dauka kan El-Rufai.

A cewarsa, El-Rufai ya shiga jam’iyyar ne ta bayan gida kuma tun a ranar 3 ga watan Afrilu, 2025 an bayyana cewa duk wanda ke son shiga jam’iyyar sai ya bi matakin ofishin mazaba da na jiha, amma El-Rufai bai bi wannan hanya ba. Don haka ne kwamitin kasa ya dakatar da shi har na shekaru 30, kuma wannan hukunci ba zai canza ba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata