Gwamnatin Jihar Kebbi ta sanar da cewa za a gudanar da Bikin Kamun Kifi na Duniya na Argungu daga 11 zuwa 14 ga Fabrairu na wannan shekara.
Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Mai Martaba Sarkin Argungu, Alhaji Samaila Mera ya bayyana wa ’yan jarida, bayan wani taro da aka yi da Kwamitin Tsare-tsaren Bikin na Jiha da Kwamitin Shirya Biki na Masarautar Argungu, a Ofishin Mataimakin Gwamnan Jihar Kebbi ranar Juma’a, kamar yadda Channels TV ta ruwaito.
Sarkin Argungu ya bayyana cewa bikin kamun kifin ya samo asali ne a matsayin matakin samar da zaman lafiya tsakanin ’yan jihadin Daular Usmaniyya ta Sakkwato da Masarautar Kanta, kafin daga bisani ya zama wani babban bikin al’adu.
Ya ƙara da cewa, saboda muhimmancin tarihin bikin, UNESCO ta amince da shi a matsayin bikin al’adu na kasa da kasa, sannan bayan Yaƙin Basasar Nijeriya, an yi amfani da bikin wajen ƙarfafa haɗin kan ƙasa da zaman lafiya.
Jihar Kebbi ta ayyana 11 da 14 ga Fabrairu a matsayin ranakun bikin Kamun Kifi na Argungu na duniya
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
