Sunday, April 5, 2026
HomeSiyasaJihohin APC sun sake mara wa Tinubu baya matsayin dan takara a...

Jihohin APC sun sake mara wa Tinubu baya matsayin dan takara a zaɓen 2027

Jam’iyyar APC a jihohi da dama ta sake bayyana goyon bayanta ga shugaba Bola Tinubu, a matsayin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar a zaben 2027.

Rahoton Daily Trust ya ce tarukan zaɓen shugabannin jam’iyyar da aka gudanar a jihohi da dama ranar Talata sun jaddada wannan matsaya, inda jihohi kamar Kaduna, Gombe, Kebbi, Taraba da Edo suka sabunta kiran Tinubu ya tsaya takara karo na biyu.

A jihar Kaduna, Gwamna Uba Sani ya ce jam’iyyar za ta hada kai domin tabbatar da nasara daga matakin mazabu har sama.

Shugaban majalisar wakilai, Abbas Tajudeen, ya bukaci sabbin shugabannin APC na jihar su samar wa Tinubu akalla kuri’u miliyan biyu a 2027.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata