Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiJihohin da ke son rage kudin wutar lantarki dole su biya tallafi...

Jihohin da ke son rage kudin wutar lantarki dole su biya tallafi – Hukumar NERC

Hukumar kula da lantarki ta Nijeriya (NERC) ta bayyana cewa gwamnatocin jihohi ba su da ikon mallakar rumbun wutar lantarki ta kasa (national grid) ko kuma tashoshin wutar lantarki da aka kafa bisa dokokin tarayya ko wadanda ke aiki da lasisin da hukumar ta bayar.

Hukumar ta fadi hakan ne a cikin wata sanarwa da ta fitar domin mayar da martani kan cece-kuce da ya biyo bayan matakin Hukumar Lantarki ta Jihar Enugu da ta rage kudin wutar Band A.

A cikin wata sanarwa a ranar Alhamis, hukumar NERC ta bukaci gwamnatocin jihohi da su sanya farashin wutar da ya yi daidai da kudin sayen wutar gaba daya ko kuma su shirya su biyan tallafi idan suka rage farashin fiye da yadda ya kamata.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata