Rundunar Sojin Sama ta Nijeriya ta tabbatar da cewa jirgin ta kirar C-130 mai lamba NAF 913 ya isa cibiyar gyara jirage ta OGMA da ke Lisbon lafiya a Portugal a ranar 26 Disamba, 2025.
Wannan na zuwa ne bayan da Burkina Faso ta tsare jirgin da ma’aikatansa a baya bisa zargin keta sararin samaniyarta a ranar 8 ga watan Disamba.
Rundunar ta ce jirgin ya kammala tafiyar ferry flight bisa sabon tsarin tashi da ka’idojin tsaron jiragen sama, inda ya bi ta Banjul da Casablanca ba tare da wata matsala ba.
Kakakin rundunar sojin sama ta Nijeriya Air Commodore Ehimen Ejodame ya bayyana cewa dukkan ma’aikatan suna cikin koshin lafiya, tare da gode wa hukumomin kasashen da aka bi ta cikinsu bisa hadin kai da goyon baya.
