A wata hira da gidan talabijin na Channels, an jiyo Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfa na cewa kiran da APC da wasu ke yi masa tamkar karkatar da hankali ne, domin a zaben 2023 ma duka manyan jiga-jigan APC sun hada kai amma bai hana shi samun nasara ba.
Rahoton Jaridar Daily Trsut ya Ambato gwamnan na cewa “Ina addu’ar Allah ya sa Matawalle ya sake tsayawa takara a 2027. Kafin karfe 10 na safe, insha Allah, zan gama da shi,”.
Ya ce bai jin tsoron kowane dan takara, domin iko daga Allah ne, kuma har yanzu ba a ga wani sauyi daga wajen Matawalle da zai ba shi rinjaye.
Kan rikicin cikin gida da sauya sheka zuwa ADC, Lawal ya ce babu wata jam’iyya a Najeriya da ba ta da matsala.
