Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiKare kai da wasu garuruwan ke yi na kara haddasa matsaloli maimakon...

Kare kai da wasu garuruwan ke yi na kara haddasa matsaloli maimakon magance su a jihar Filato – Rundunar sojin Nijeriya

Rundunar Sojin Najeriya ta ce barin al’ummomi su kare kansu daga maƙiya ba ya magance rikice-rikicen da faruwa a jihar Filato, illa ƙara tsananta su.

Babban daraktan hulɗar sojoji da fararen hula, Manjo Janar MA Etsy-Ndagi, ya bayyana haka ne a Jos, yana mai cewa tsarin bai taba haifar da da mai ido ba.

A cewarsa, rikicin manoma da makiyaya ya koma salo na hare-hare da ramuwar gayya, inda kowane ɓangare ke zargin ɗaya da farauta ko lalata dukiya.

Hakazalika ya ce dole ne a kwace dukkan makamai kowane iri domin a sami zaman lafiya mai ɗorewa kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Etsy-Ndagi ya jaddada cewa sojoji ba sa goyon bayan al’ummomi su ɗauki doka a hannunsu, sai dai suna kare garuruwan da ke fuskantar tashin hankali. Ya kuma yi kira ga mazauna Filato da su zauna lafiya su kuma ba ƙungiyoyin tsaro hadin kai.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata