Hukumar Alhazan Nijeriya NAHCON, ta ce ta yi nasarar jigilar maniyyata 32,549 a jirgi, wanda ya kai kashi 79.1% na adadin maniyyatan da ke shirin gudanar da aikin Hajjin shekarar 2025.
A wata sanarwa da mataimakiyar daraktar yada labarai da ta hukumar, Fatima Sanda Usara ta fitar, ta ce an samu nasarar ne bayan fara gudanar da aikin jigilar a ranar 9 ga watan Mayun 2025.
Daily Trust ta ruwaito cewa ‘yan Nijeriya 42,000 ne ake sa ran za su halarci aikin hajjin na wannan shekarar shekara.
