Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiKashim Shettima ya kai ziyarar ta’aziyya Ilorin kan harin Kaiama

Kashim Shettima ya kai ziyarar ta’aziyya Ilorin kan harin Kaiama

Mataimakin Shugaban Nijeriya, Kashim Shettima, ya isa birnin Ilorin na Jihar Kwara domin jajanta wa gwamnati da al’ummar jihar bisa harin da aka kai wa al’ummar Woro da ke Karamar Hukumar Kaiama a ranar Talata.

Kamar yadda gidan talabijin na Channels ya ruwaito, jirgin Mataimakin Shugaban ya sauka a Filin Jirgin Sama na Janar Tunde Idiagbon da misalin karfe 10:30 na safiyar Asabar, inda ya zo domin nuna alhini da duba halin tsaro.

Mataimakin Shugaban ya samu rakiyar Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum, Sanata Ali Ndume, da Sanata Ovie Omo-Agege zuwa jihar.

A filin jirgin saman, Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, tare da Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kwara, Yakubu Salihu, da Sanatan Kwara Ta Arewa, Sadiq Umar, ne suka tarbe shi.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata