Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiKiris ya rage na ajiye mukamina na minista a lokacin Buhari -...

Kiris ya rage na ajiye mukamina na minista a lokacin Buhari – Lai Mohammed

Tsohon Ministan Yaɗa Labarai da Al’adu, Alhaji Lai Mohammed, ya bayyana cewa ya kusan yin murabus a wani lokaci da ya kira mafi wahala a lokacin mulkin marigayi Shugaba Muhammadu Buhari.

Ya bayyana haka ne a Abuja yayin ƙaddamar da littafinsa mai taken “Headlines & Soundbites,” inda ya ce kasancewarsa a tsakiyar harkokin gwamnati na tsawon shekaru takwas ya ɗora masa nauyin fayyace gaskiya da gyara fahimtar da aka yi kuskure game da mulkin Buhari.

Mohammed ya ce littafin ya bayyana yadda aka tafiyar da sadarwar gwamnati a lokutan rikici, labaran ƙarya da matsin lamba, yana mai jaddada cewa ‘yan Afirka su ne ya kamata su ba da labarin kansu.

A taron, Ministan Yaɗa Labarai na yanzu, Mohammed Idris, ya yaba da rawar da Lai Mohammed ya taka, yayin da Halima Buhari ta ce mahaifinta yana sane da suka da yabon da ake yi wa gwamnatinsa a lokacin mulki.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata