Tuesday, April 7, 2026
HomeLabaraiKiristocin da aka yi garkuwa dasu a jihar Kaduna sun shaki iskar...

Kiristocin da aka yi garkuwa dasu a jihar Kaduna sun shaki iskar ‘yanci

Kiristocin da aka sace suna tsaka da ibada a garin Kurmin Wali da ke karamar hukumar Kajuru a jihar Kaduna sun shaki iskar ‘yanci.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa guda daga cikin jagororin yankin da ya bukaci a sakaya sunansa, ya bayyana cewa an saki Kiristocin ne a ranar Alhamis.

A ranar 18 ga watan Janairun 2026 ne aka yi awon gaba da kusan mutane 177 yayin da suke tsaka da ibada a coci, sai dai rahotanni sun bayyana cewa 80 daga cikin su sun tsere daga baya.

Har zuwa wannan lokaci dai babu tabbaci kan ko an biya kudin fansa kafin a sake su, da kuma adadin wadanda suka dawo gida, kana kuma babu wata sanarwa daga gwamnatin jihar ko hukumomin tsaro.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata