Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiKokar su Wike daga PDP ba zai magance matsalarta ba - Celeb...

Kokar su Wike daga PDP ba zai magance matsalarta ba – Celeb Muftwang

Gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang, ya nesanta kansa daga matakin jam’iyyar PDP na korar Ministan Abuja, Nyesom Wike, da tsohon Gwamnan Ekiti, Ayodele Fayose, da sauran manyan jiga-jigai da aka zarga da yi wa jam’iyyar zagon kasa.

A cikin wata sanarwa da daraktan yada Labaran gwamnan Gyang Bere ya fitar, Mutfwang ya bayyana cewa wannan batu ba a tattauna shi ba a taron Gwamnonin PDP kafin a gabatar da shi a gangamin jam’iyyar da ake gudanarwa a Ibadan.

Ya ce matakin da aka dauka bai dace ba, kuma ba shi ne hanya mafi dacewa don magance rikicin jam’iyyar ba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata