Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiKotu a Marocco ta yanke wa magoya bayan Senegal da suka ta...

Kotu a Marocco ta yanke wa magoya bayan Senegal da suka ta da tarzoma a gasar AFCON 2025 hukunci

Wata kotu a ƙasar Morocco ta yanke wa magoya bayan Senegal 18,hukunci bisa laifin ta da tarzoma a wasan karshe na cin kofin Nahiyar Afrika na 2025.

An same su da laifin tayar da hankali da lalata wasu kayayyaki bayan sun kutsa cikin filin wasa, suka jefa kujeru, tare da arangama da jami’an tsaro sakamakon bugun fanareti da aka bai wa ƙasar mai masaukin baki.

Duk da cewa Senegal ta doke Morocco da ci 1–0, tarzomar ta jawo asarar fiye da dala $476,000, kuma an dakatar da wasan na ɗan lokaci.

Kotun ta yanke wa mutum 11 hukuncin ɗaurin shekara guda, mutane huɗu watanni shida, sai wasu huɗu watanni uku.

Lauyoyin masu laifin sun ce hukuncin ya yi tsauri, kuma sun bayyana aniyar ɗaukaka ƙara.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata