Babbar kotun birnin tarayya Abuja ta bayar da belin Sanata mai wakiltar mazabar Kogi ta tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan a kan kudi naira miliyan 50, bayan ta ki amsa laifin bata suna da ake zarginta da shi.
Kotun ta kuma ba da sharadin gabatar da mutum daya da zai tsaya mata wanda dole ne ya kasance mai gaskiya kuma ya mallaki kadarori a cikin Abuja.
Alkalin kotun Justice Chizoba Orji ya dage sauraren karar zuwa ranar 23 ga Satumba, 2025.
Tun da farko, gwamnatin tarayya ta gurfanar da ‘yar majalisar a gaban kuliya bisa tuhume-tuhume guda uku da suka shafi bata sunan shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio da tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello.
