Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiKotu ta bai wa hukumar kula da masu yi wa kasa hidima...

Kotu ta bai wa hukumar kula da masu yi wa kasa hidima a Najeriya ta NYSC umarnin barin mata su rika sa siket

Salisu Ado Sulaiman

Babbar kotun tarayyar Najeriya da ke zaman ta a jihar Legas, ta bai wa hukumar kula da masu yi wa kasa hidima NYSC umarnin barin mata su rika sa siket bisa dalilan da suka shafi addini.

Yayin da take yanke hukunci a ranar 13 ga watan Yuni, mai shari’a Hauwa Yilwa, ta ce tilastawa mata saka wando da hukumar ke yi ya saba wa tanadin kundin tsarin mulkin Najeriya, na ‘yancin gudanar da addini da kuma mutunci.

Tun da farko dai, wasu mata da suka kammala yi wa kasa hidima su biyu, Ogunjobi Blessing da Ayuba Vivian ne suka shigar da karar hukumar a lokuta daban daban, inda mai shari’a Hauwa Yilwa ta yanke hukunci bai daya.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata