Wasu manyan kotuna a Abuja guda biyu sun gayyaci shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, da Sanata Onyekachi Nwaebonyi, bisa zargin bata suna, cin zarafi, da kuma take hakkin sanata Natasha Akpoti-Uduaghan.
A karar mai lamba FCT/HC/CV/754/2025 a gaban mai shari’a Abubakar Idris Kutigi, kotun ta ba Akpoti-Uduaghan izinin mika takardar sammaci da duk wasu matakai da suka hada da sauraran karar da Sanata Akpabio,da Sanata Onyekachi, cikin sammacin akwai babban mai taimaka wa Akpabio, Mfon Patrick, da magatakardar Majalisar dattawa.
Mai shari’a Kutigi ya sanya ranar 9 ga watan Yuni, 2025, domin sake yin zama kan shari’ar.
