Babbar kotun tarayya da ke Legas ta salami Ayodele Fayose daga dukkan tuhume-tuhumen halatta kudade da Hukumar EFCC ta shigar da shi.
Mai shari’a Chukwujekwu Aneke ya amince da bukatar Fayose na cewa babu laifi a kansa, yana mai cewa EFCC ta kasa gabatar da hujjojin da za su tabbatar da laifinsa.
Fayose ya fuskanci shari’a ne kan zargin karkatar da kudade da cin hanci a lokacin da yake gwamnan Jihar Ekiti kamar yadda rahoton jaridar Daily Nigerian ya tabbatar.
