Kotun tarayya da ke Abuja ta ɗage shari’ar tsohon ministan shari’a, Abubakar Malami, tare da ɗansa Abdulaziz, zuwa 27 ga Fabrairu, 2026.
Alƙaliyar kotun, Joyce Abdulmalik, ta ɗauki wannan mataki ne sakamakon hutun da ministan Abuja, Nyesom Wike ya bayar gabanin zaɓen kananan hukumomin Abuja.
Rahotanni sun nuna cewa a safiyar ranar shari’ar, ma’aikatan kotu kaɗan ne suka halarta, kuma babu lauyoyi ko ɓangarorin shari’ar da suka bayyana a kotun.
