Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiKotun Amurka ta daure wasu 'yan Nijeriya 5 tsawon shekaru 159 bayan...

Kotun Amurka ta daure wasu ‘yan Nijeriya 5 tsawon shekaru 159 bayan ta same su da laifin damfara

Wata kotu a kasar Amurka ta yanke wa wasu ‘yan Nijeriya biyar hukuncin daurin shekara 159 a gidan yari bisa samunsu da laifin damfarar Amurkawa, kamfanoni da hukumomin gwamnati sama da 100 kudaden da suka kai dala miliyan 17.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da jaridar Punch ta samu a shafin yanar gizo na ma’aikatar shari’a ta Amurka a ranar Laraba, mai dauke da sa hannun mukaddashin babban lauyan Amurka na gundumar Gabashin Texas, Ray Combs.

Sanarwar ta kara da cewa wadanda ake tuhumar, Damilola Kumapayi, Sandra Iribhogbe, Edgal Iribhogbe, Chidindu Okeke da Chiagoziem Okeke, na cikin wani gungun ‘yan damfara na kasa da kasa

Lauyan ya bayyana cewa wadanda ake tuhumar sun fara wannan harkalla ne a shekarar 2017 ta hanyar damfarar tsofaffi.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata